Muhammadu Korau
Gabatarwa
Sarkin Katsina Muhammadu Korau, shi ne sarki na shida a jerin sarakunan Katsina. Shi Sarki Muhammadu Korau Haɓe ne kuma Musulmi. Ya zo a ruwayar Ingawa (2006), cewa shi Sarki Muhammadu Korau ɗan asalin garin Tsafe (Chafe) ne wacce ke cikin Jahar Sakkwato ta yau. Sarki Muhammadu Korau ya hau gadon sarautar Katsina bayan da ya kayar da sarki Sanau a kokawar da suka buga.
A zamanin sarki Korau ne aka gina masallacin juma’a na farko a garin Katsina, wanda shi wannan masallaci daga baya ya bunƙasa ya koma wata babbar jami’ar karantar da addinin Musulunci. A cikin wannan masallaci akwai wata hasumiya mai tsawo wacce ake yiwa laƙabi da Hasumiyar Gobarau.
Manazarta:
Ingawa T.L. (2006). Katsina a History of an Ancient City. Hamdala Prinitng and Publishing.
Lugga S.A. (2004). Katsina College. Lugga Press, Katsina
Mamman M. (2015). Tarihin Unguwannin Birnin Kastina. Ahmadu Bello Univeristy Press Ltd, Samaru, Zaria-Nigeria.
Sarakunan Katsina
Haɓawa:
Fulani:
- Tarihin Katsina
- Gidan Korau
- Hasumiyar Gobarau
- Sanau da Korau
- Kwalejin Katsina
- Durɓi ta Kusheyi
- Hukumar Gargajiya
Ƙofofin Katsina
- Ƙofar Guga
- Ƙofar ‘Yanɗaka
- Ƙofar Ƙaura
- Ƙofar Durɓi
- Ƙofar Sauri
- Ƙofar Turmi
- Ƙofar Keke
- Ƙofar Angulu
- Ƙofar Gazobi
- Ƙofar Ƙwaya
- Ƙofar Waziri
- Ƙofar Soro
- Ƙofar Marusa
Tura wannan shafi zuwa ga abokai ta:
TweetLatsa madannin "Like" ka nuna goyon baya ko kuma "Share" ka yaɗa shafin